* Ɗãkunan Allah a cikin ƙasa dõmin mutãne su yi ibãda zuwa gare su biyu ne; Ka'aba a Makka da Baitil Muƙaddas. An gina Ka'aba a gabaninsa da shekara arba'in. Dãkin Bakka kuwa Ibrãhĩma ne ya gina shi alhãli Yahũdu da Nasãra sunã cewa kan addininsa suke. Dã sunã faɗar gaskiya dã sun kõma a gare shi gabã ɗaya. ** Ana ce wa Makka Bakka.