* Kisan da aka yi musu, Allah ne Ya kashe su, haka Annabi ya ɗebi tsakuwa da hannunsa mai daraja ya jefa wa kãfirai, tsakuwar ta shiga cikin idãnun kõwane ɗaya daga cikinsu. To, wannan jĩfar daga Allah take. Sabõda haka duk ganĩmar dai ta Allah ce da ManzonSa, sai yadda Ya so, zã a raba ta.