* 'Ya'yansa-Yanã nufin mãtan aurensu, dõmin kõwane Annabi uban al'ummarsa ne.Bã ya kamãta a ce wai yanã kiran mazan gari zuwa ga 'ya'yansa uku, dõmin bãbu wata shari'a ta Allah, ga saninmu, wadda ta halattã haɗuwar mazã biyu ko fiye da biyu a kan auren mace guda.
* Ya faɗi haka dõmin bã shi da dangi a cikin su. Daga gare shi ba a kuma aiko wani Annabi ba sai a cikin wadãtar dangin sa.