* Ya ambaci hũdu da mutãnensa Ãdãwa da misãlin waɗansu mãsu garagaɗi daga Annabãwan da suka shũɗe da kuma mutãnensu da yadda aka halaka su daga inda suke zaton rahama ta Je musu. Haka ne hukuncin. Dukan wanda aka yi wa gargaɗi da bin umurnin Allah, idan ya ƙi bi, sa'an nan ya bi son zũciyarsa, Allah zai Kãwo masa azãba daga inda yake zaton alheri ga kansa.
* Ya wajaba a gare su, watau sakamakonsa ya tabbata a kansu da azãba.